Sunday 13 February 2011

YADDA ZAKARUBUTA LABARIN FILM

A nan, ana so marubuci ya bayyana labarin tun daga labari a takaice, fadada labarin har zuwa wajajen (locations) da za a dauki shirin fim din.Wanda a nan ne marubuci zai bayyana halaye da dabi’un wadanda suke fim din (characters), zai kuma rubuta zantuka (dialogues) da za a yi a fim din, zai kuma rubuta wajajen da za a dauki shirin fim din.
Misali, cikin kayataccen lambu mai yawan furanni da dogayen bishiyoyi, Amin ne da A’isha suke gudanar da hirarsu ta soyayya, ana saura kwanaki uku bikinsu.
“Amarya, kin sha kamshi; amarya ba kya laifi ko da kuwa kin kashe dan masu gida.” Ya fara da zolayarta.
Dariya kawai ta yi, don ta san shi gwani ne wajen zolaya.
“Ango ka sha kamshi, ango ba da kanka a sare, ka je gida ka ce ya fadi.” Ta ce da shi bayan ’yar karamar dariyar da ta yi.
A nan marubucin ya fitar da wajen da za a dauki shirin fim din, ya kuma sanya zantukan da za a yi a wajen daukar fitowar (Scene).
Misalin halayya kuma ga su kamar haka:
Ibrahim, shiru-shiru, mai yawan fara’a. Amina, marar kunya da rashin mutunci. Karime, ballagaza marar kamun kai. Alhaji Idi, mai zafin rai, wanda ba ya so a raina shi da sauransu.
Haka a wannan rukunin ake so marubucin fim ya fitar da abubuwa kamar haka:
Lokacin daukar shirin fim (Shooting Time). Misali, safe, rana, dare, yamma da sauransu.
(i)-Wajen daukar shirin fim, wannan ya kasu kashi biyu; a ciki (Interior) da kuma a waje (Edterior). Misali, a ciki, akwai daki, falo, cikin mota da makamantansu. Misalin a waje, akwai kan titi, a daji, a farfajiyar wani waje, da sauransu. Don haka ne ake son marubuci ya tantance inda za a yi daukar shirin fim.
(ii)-Tsarin daukar hoto (Scene List or Scene Number).
A nan, ana so marubucin fim ya fitar ko ya tsara yadda za a dauki fim, wanda zai bayar da lambar daukar hoto ne ga kowace fitowa (Scene Number).
(4)-Tsarin yadda za a dauki labarin fim da kyamara (Shooting Script).
A nan, marubuci zai rubuta tsarin yadda za a dauki shirin fim ne, ta hanyar yin amfani da zirga-zirgar kyamara ta bangaren:
(4a)-Kusurwar Hange (Angle of biew).
Ana so marubuci ya rubuta kusurwar hangen da yake so kyamara ta kasance tsakaninta da abin da ake dauka (Subjet) ko inda aikatau (Action) ke faruwa. Misali, kasa-kasa ne (Low Angle); daga sama ne (High Angle) ko kuma saitin ido (Eye-Lebel Angle) ko zuwa rabin jiki (Portrait), ko kuma gaba daya surar mutum ko gaba daya inda aikatau ke faruwa (Complete Subject or Action).
(4b)-Fagen Hange (Field of biew).
A nan, ana so marubuci ya bayyanar da nisan ko tazarar da ke tsakanin kyamara da abin da take dauka (Subject), ko kuma inda aikatau ke faruwa (Action). A nan ake bayyana cewa daukar kusa-da-kusa ne (Close Shot), ko daukar nesa (Long Shot), ko kuma matsakaicin dauka ne (Medium Shot), ko juya kyamara za a yi (Upside Down).
(4c)-Zirga-zirgar kyamara (Camera Mobement).
Ana so marubucin fim ya zayyana yadda kyamarar za ta rika zuwa da komayya ga abin da take dauka (Subject), ko inda aikatau ke faruwa (Action). Idan mutum ya kalli saman daki ko sararin samaniya ko dai wani abu da ya fi mutum tsayi, ko za a daga kyamara zuwa kallon sama, to marubucin zai bayyana cewa kyamara za ta gyada kai (Tilting). Haka idan mutane suna da yawa kuma ana daukar su a shirin fim, idan suna magana, a nan kyamara yawanci waige-waige take, saboda lokacin da suke magana kyamarar za ta rika daukar mai magana; shi ya sa ake so marubucin ya bayyana duk irin waige (Pan) da kyamara za ta yi yayin daukar shirin fim. Ko kuma kyamarar za ta zauna a kurar daukar hoto ne (Dolly).
(4d). Yanayin sadarwa don bambamcewa daga dauka zuwa dauka, ko daga fitowa zuwa fitowa. A nan, marubuci kan rubuta ko tsara yadda yake son hakan ya gudanu. A cikin yanayin sadarwa akwai hoton da zai dinga daukewa ne kamar daiman (Diamond), dusashewa (Fading), narkewa (Dissolbing), rugujewa (Shattering), wannan ya kasu kashi da yawa. Wani kan yi dama (Right), hagu (Left), sama (Up), ko kasa (Down). Wani nau’in sadarwar tsakanin dauka da dauka kan zo da tafiyar tsutsa (Zig-Zag), wanda ya kasu kashi biyu, a kwance (Horizontal) ko a tsaye (bertical) da sauransu.
Sanin ka’idojin rubutu kafin rubuta labarin fim
Yana da kyau, ya kuma zama wajibi marubucin labarin fim ya san ka’idojin rubutu, wanda ta haka ne kawai za a iya fitar da ma’anonin zantuka a cikin labarin fim.
Misali, Musa ya tafi gida. Musa ya tafi gida? Ka ga jimla ta farko ta nuna cewa Musa ya riga ya tafi gida (Statement). Amma jimla ta biyu, tambaya take shin ko Musa ya tafi gida? Ka ga ke nan, idan marubuci bai san ka’idojin rubutu ba, to zai matukar ba wa ’yan wasa ciwon kai, kuma shirin zai samu nakasu. ka’idojin rubutu da suka kamata marubucin fim ya sani sun hada da Aya (.) (Fullstop), Wakafi (Comma) (,), Alamar motsin rai (!) (Edclamation Mark), Alamar tambaya (kuestion Mark) (?), Ruwa Biyu (Colon) (:), Baka Biyu {( )}, Alamar zancen wani (‘ ’ ko “ “), Sanda-Jirge (/) da sauransu.
Ta hanyar wadannan ka’idojin rubutu ne kawai, labarin fim zai fita sumul, ba tare da Doma-Dol ko kuskure ba.

Misbahu M. Ahmad

Fitaccen mawakin Hausa na zamani kuma dan wasan fina-finan Hausa, Misbahu M. Ahmad ya auri fitacciyar ’yar wasa, Maryam Aliyu Umar. An daura auren ne a ranar Juma’a da ta gabata, da misalin karfe goma na safe, a unguwar Gwammaja, kusa da gidansu ango Misbahu, a cikin birnin Kanon Dabo.
Auren da aka daura shi a kan sadakin Naira dubu hamsin, wanda kuma aka biya lakadan ba ajalan ba, ya dauki hankalin mutane sosai, musamman ma ganin cewa wannan ba shi ne auren angon da amaryar na farko ba. Ita dai amarya Maryam, wacce kyakkyawa ce, ’yar asalin kasar Nijar, daga kabilar Bugaje, ta taba auren fitaccen dan wasa Shu’aibu Lawan, wanda aka fi sani da lakanin Kumurci a fina-finan Hausa. Kodayake auren bai yi tsawon kwana ba, ya mutu shekaru biyu da suka gabata.
Shi kuwa angon nata, Misbahu Ahmad, wanda fitaccen mawakin zamani ne na Hausa, ya taba yin aure kodayake ba ’yar fim ba ce ya aure. Kafin auren nasa na farko, ya yi kokarin auren fitattar ’yar wasa, Rukayayya Umar Santa, wacce aka fi sani da lakanin Dawayya, amma haka ba ta samu ba, duk da cewa suna kaunar juna sosai.
Fitattu daga cikin ’yan wasan fim da suka halarci daurin auren, sun hada da fitaccen mawaki, Aminu ALA da mawaki Mudassir Kassim da Ibrahim Mandawari da Abdulhadi (Awilo). Sauran sun hada da Baba karami da sauransu da dama da suka halarci auren.
Kafin ranar daurin auren, a ranar Laraba, 16 ga wannan watan, tawagar anguna da ta amare, sun tattaru a otel din Alliance France da ke birnin Kano, da dare, inda suka gudanar da kwarya-kwaryan biki. ’Yan wasa da suka samu halartar bikin kuma suka taka rawa sun hada da Rashida Adamu Abdullahi da Abubakar Baballe Hayatu da Hauwa Ali Dodo, wacce aka fi sani da lakanin Biba Problem da kuma Daso. Sauran sun hada da Lubabatu Madaki da Tahir I. Tahir da mawaki Adamu Nagudu da Umar Gombe da Fauziyya Mai Kyau da Maimuna HRB da Salisu Gombe, da sauransu.
A wurin shagalin, an gabatar da kade-kade da raye-raye, sannan kuma maza da mata sun yi kwalliya da shigar Buzaye, kasancewar amaryar ’yar kabilar Bugaje ce.

BABALLE HAYATU A TSINSIYA

Wane fim din Hausa ne ya kunshi mutane fiye da dari takwas wadanda kowannensu yana da rawar da yake takawa a cikin fim din? Wane fim din Hausa ne ya kunshi kabilu dabam-dabam na Nijeriya a cikinsa? Wane fim din Hausa ne wanda a saboda muhimmancinsa wajen yunkurin hada kan al'umma har ofishin jakadancin Amurka dake Nijeriya ya ga ya dace ya dauki nauyin shirya shi? Wane fim din Hausa ne Baballe Hayatu da Francisca Isaac suke fitowa ciki a zaman manyan jarumai?
Amsar wadannan tambayoyin da wasunsu duk kwaya daya ce tak: Tsintsiya!
Hausawa suka ce tsinken tsintsiya ba ya iya shara, sai an hada su da yawa suka zamo tsintsiya guda, suka yi aiki tare sannan zasu iya share dauda. Wannan ita ce ma'anar wannan sabon fim wanda kamfanin Alhaji Hamisu Lamido Iyan-Tama yake dauka a yanzu haka, wanda kuma nan da 'yan watanni kadan zai fito.
Filin "A Bari Ya Huce..." ya tattauna wannan sabon fim da Alhaji Sani Mohammed, jami'i a sashen hulda da jama'a na Ofishin Jakadancin Amurka a Abuja, Nijeriya, da kuma Alhaji Hamisu Lamido Iyan-Tama, mai kula da shirya fim din.
Alhaji Sani Mohammed ya bayyana wannan fim da cewa, "Tsintsiya wani nau'in fim ne na Hausa irin (wan)da kila za a iya cewa a a taba yin irinsa ba..." Shi kuwa Iyan-Tama, cewa yake yi, "...labarin (dake cikin) Tsintsiya, abu ne da zai amfani al'ummar yanzu, da al'ummar da zata zo gaba..."
Shi dai wannan fim na Hausa na "Tsintsiya" ya samo asalinsa ne daga wani fim na turanci mai suna "The West Side Story" wanda ya kunshi labarin wasu kungiyoyin banga su biyu masu fada da juna a New York a zamanin baya, da yadda aka yi soyayya ta sa suka sasanta da junansu suka zamo tsintsiya guda.
A matsa sama domin jin kashin fariko da na biyu na tattaunawar da wannan fili yayi da jami'an biyu dangane da wannan sabon fim Tsintsiya.

BAYANI DAGA BAKIN WASU DAGA YANWASAN HAUSA

Mutane masu fasaha da fikirar kirkira, musamman ma mawaka da ’yan wasan kwaikwayo na Hausa, a duk lokacin da suka furta wani abu, sukan haddasa nishadantarwa ko kuma fadakarwa. A ’yan kwanakin nan, mun tattauna da irin wadannan masu sana’a, kuma ga guda goma daga cikinsu, da kuma irin abubuwan da suka furta da bakunansu, a kan al’amura daban-daban.
(1)-Umar Nagudu, mawakin Hausa na zamani. An tambaye shi cewa: To, ko za ka gaya mana abin da ya ba ka sha’awa har ka shiga sana’ar wakar Hausa? Ya amsa da cewa:
“Abin da ya ja hankalina har na ga cewa ya kamata in shiga harkar waka shi ne, idan ina sauraren wakokin wasu mawakan, nakan yi la’akari da irin sakonnin da suke aikawa ga al’umma, wanda haka ya sanya har ma mutane kan zama sun fadakantu daga darussan wadannan wakoki. Wannan ne ya ban sha’awa kuma na ga cewa ni ma ya dace in shiga cikin harkar domin in ba da tawa gudunmowa ga al’umma.”
(2)-Haruna danjuma (Mutuwa Dole). An tambaye shi cewa: Yaushe ne ka fara wasan kwaikwayo? Ya amsa da cewa:
“Na fara wasan kwaikwayo tun ina makarantar firamare, ina dan shekara 11. Na shiga firamare ina dan shekara 7, na shekara 4 ina aji hudu, muka fara wasan kwaikwayo. Tun muna yi tsakaninmu yara har ya zamanto muna yi a gidan masaukin baki, domin a lokacin mulkin En-e En-e, muna zuwa gidan muna yin wasannin; inda yara kan biya ’yan kudi su kalla. Har daga nan na samu hikimar yanke hotunan Kaboyi, ina yin silima nawa a gida, ina samun katon na suga da fitilar A-ci-bal-bal, yara na biyan kudi suna kallo, a zauren gidanmu.”
(3)-Hussaini BBC. An tambaye shi cewa: Baya ga daukar hoto, na kuma ji cewa kai mawaki ne, to yaya ka shiga harkar waka? Ya amsa da cewa:
“Gaskiya fisabilillahi, ina yin harkar waka, sai dai na fi karfi a wakokin yabon manzon Allah. Amma yanzu ina yin ta siyasa, don an fi sanina a harkar wakar siyasa. Na shiga harkar wakar siyasa don in fadakar da talakawa da al’umma, kan cewa su rika zabar abin da zai fitar da su daga cikin kunci, ba wai masu yi musu karyar zan yi kaza, zan yi kaza ba.”
(4)-dan Auta (Mai wasan barkwanci). An tambaye shi cewa: Akasarin wasanninka, kana nuna wauta a ciki. Ko me ya sa kake yin irin wannan fita tare da jero maganganu wasu na bin wasu, to rubutawa kake yi ne ko yaya kake yi? Shi kuma ya amsa da cewa:
“Wasan kwaikwayo da ban dariya ko wauta, na sanya mutane sha’awar kallon abin da ake yi, su kuma dauki darasi daga ciki. Kuma abu ne daga Allah, ba na rubuta komai. Ina fadi ne kurum a jere har mutane su gamsu. Kuma ina yin wannan wasa ne a ko’ina aka gayyace ni.”
(5)-Hamisu Lamido Iyan-Tama (Mai shirya fina-finai kuma dan wasan Hausa). An tambaye shi cewa: Ko akwai wani abu takamaimai da ya faru a tsakaninku da Biba Problem, kamar magana ko wani al’amari, wanda za ka iya tuna ta da shi da zarar an ambaci sunanta? Ya amsa da cewa:
“Marigayiya Hauwa Ali Dodo, akwai wani abu da ya faru tsakanina da ita, wanda nakan tuna ta sosai a kansa. Wannan al’amari kuwa shi ne, a duk lokacin da muka hadu da ita, takan kira ni da wani suna, ni ma nakan kira ta da wani suna. A duk lokacin da muka hadu, sai ta fara kira na da wannan suna, sannan ni ma in kira ta da nata sunan, sannan mu fara magana. Watau a duk lokacin da muka hadu, za ka ji ta kira ni da cewa: “Zagadada!” Ni kuwa sai in ce mata: “Haba Hauwa’u? Ai tun da kin auri mai arziki sai ki rike kudin ni kuma in tafi…” Da zarar mun fadi haka ga juna, sai ta kyalkyace da dariya. Wannan al’amari, ba na mantawa da shi a duk lokacin da batun Hauwa Ali Dodo ya fado mani a rai.”
(6)-Carmen McCain (Talatu Baturiya). An tambaye ta cewa: Ko za ki yi mana bayanin yadda aka yi ma kika samu kanki wajen sha’awar magana da harshen Hausa, wanda a yanzu kin zama babbar daliba da ke koyo da nazartar harshen? Ta amsa da cewa:
“Idan kana nufin yadda ma na fara koyon harshen Hausa ne, sai in ce maka ni na girma ne a garin Jos, domin kuwa babana Farfesa ne a Jami’ar Jos. Lokacin da nake zaune da iyayen nawa a Jos ne na fara dan koyon magana da harshen. Na fara da koyon gaisuwa, irin kamar ‘Sannu, ina kwana?’ da dai irin wadannan maganganu da ake yi na yau da kullum, musamman ma idan na je kasuwa. Amma lokacin da na koma Amurka, na fara karatun digiri na biyu a Jami’ar Wisconsin, sai suka ce mani ya zama dole in dauki wani kwas na musamman kan nazarain harsunan Afrika,. Dalili ke nan na tuna da cewa, ina iya magana kadan-kadan da harshen Hausa, don haka zan ci gaba da nazarin harshen ma gaba daya. Tun daga nan na fara halartar kwasa-kwasan Hausa a nan jami’ar, inda daga bisani da na zo Najeriya, sai na je Sakkwato, inda na ci gaba da koyon harshen na Hausa. Amma a lokacin, malamina, Dokta Malami Buba, a lokacin nan yana Jami’ar Usman danfodiyo, shi ne ya kawo mani fina-finai da littattafan Hausa, na fara karanta littattafan da kuma kallon fina-finan, wannan shi ya kara ba ni sha’awa da kwarin gwiwar son harshen, domin a da, ina nazarin harshen ne saboda dokar da aka ba ni a jami’a ne kawai, ina tunanin zan yi rubutu kan  littattafan Najeriya, amma da Turanci, sai dai na san zan dawo Najeriya domin in yi amfani da shi, amma ba na tunanin zan yi amfani da shi a bincike na. Amma lokacin da na fara kallon fina-finan Hausa, kuma na fara karanta littattafan Hausa, sai na ce dole ne ma in fara bincike a kansa, domin kuwa akwai mutane da yawa a waje, wadanda ba su san ma cewa akwai ayyukan fasaha na Hausa ba. Haka kuma, wasu na cewa babu bunkasuwar karance-karance a kasar Hausa, ni kuwa sai na ga ba haka ba ne, domin na ga cewa akwai mutane da yawa da ke kallon fina-finan Hausa kuma suke da sha’awar littattafan Hausa, dalili ke nan ya sanya na ga ya kamata in yi nazari a wannan fanni.”
(7)-Shehu Ajilo danguzuri. An tambaye shi cewa: An ce kana da alaka da marigayi Dokta Mamman Shata Katsina, ko za ka yi mana bayani game da dangantakarka da shi? Ya amsa da cewa:
“Muna da alaka da Shata, musamman don kauna, ina daya daga masu kaunar kalmominsa da abubuwan da yake fadi. Akwai lokacin da makada da mawaka da maroka suka hada wata kungiya, musamman saboda adawa da gaba da Shata. Da farko ina tare da su, har zuwa lokacin da aka je wani taro Kaduna, aka ce za a ba ni Sakatare. Na ce ba ni so, aka ce za a ba ni Ma’aji, na ce ba ni so, aka ce za a ba ni shugabanci, na ce ba ni so. Bisa ga haka wani cikinsu ya kebe ni, ya ce me ya sa ba ni son mukami a kungiyar? Na ce saboda na ga cewa ba don Allah aka kafa kungiyar ba, an kafa ta ne saboda a yi gaba kuma a musguna wa wani mutum daya kuma duk inda ka ce sai ka ci mutuncin wani, to ka jira Allah; koda Kafiri ne kuwa, bare Shatan nan Allah Ya riga Ya nuna shi ga jama’a, a duniya fiye da mu. Idan mun kai mu dubu, da an ce ga Shata, karyarmu ta kare. Dalili ke nan ya sa na kauce wa wannan kungiya. Ina nan haka, sai jarida ta fita da labarin. Da aka karanta wa Shata cewa ga abin da Ajilo ya fadi, wannan shi ne sanadin da na auri diyarsa. Marigayi Shata ya kira ni, ya ce zai ba ni Maji Dadin Shata, na ce ba ni son wannan mukamin ranka ya dade, domin rawanina a gidanka daga Allah yake. Wasu mawaka kan nemi zolaya ta, ni kuwa sai in ce masu, duk cikin mawakan Najeriya, wa ya auri diyar Shata idan ba ni ba? Don haka ni a gidan Shata Yarima ne ni, dan sarki ne ni. Wannan ita ce alakata da shi, akwai kauna tsakaninmu.”
(8)-Alkarina Ahmad Muhammad. An tambaye ta cewa: Kin ce iyayenki sun ki yarda ki shiga harkar fim, to yaya aka yi yanzu kika samu kanki cikin harkar? Ta amsa da cewa:
“Kamar yadda na gaya maka, lokacin da na shaida wa iyayena bukatata ta shiga sana’ar fim kuma suka ki yarda, na bi ra’ayinsu, sai ban shiga ba. Ni kuma ga shi ban koma makaranta ba domin ci gaba da karatuna. Bisa ga haka, akwai wani yayana, wanda ya nace yana ba ni shawarar cewa lallai ya kamata in koma makaranta. Wannan ta sanya na amince da shi, na koma makaranta. Na tafi Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Hassan Usman Katsina, inda na fara karatun Diploma kan aikin jarida. Bayan na fara karatun nan, sai na tafi Kano, na hadu da wani mutum mai suna Bashir, na nuna masa cewa ina son shiga harkar fim, watau ba tare da iyayena sun sani ba. A lokacin da na shaida masa haka, sai ya ce mani babu wani abu, domin kuwa harkar fim tasu ce, domin a daidai lokacin ma suna cikjin aikin shirya wani fim ne. Shi ne ma ya ce mani, idan zan iya zuwa, za mu tafi wajen da ake shirya fim din, domin in ga yadda ake yin komai. A lokacin sai na amince, muka tafi garin Gumel, inda Sa’idu Gwanja ke shirya wani fim dinsa, na kalli yadda ake shirya wannan fim, har ma a lokacin nan aka sanya ni na fito cikin fim din, har ma gurbin da aka ba ni da akwai waka.”
(9)-Sagolo (Mawakin Maza). An tambaye shi cewa: A cikin tsawon shekarun da ka yi kana kidan kokowa, wace kokowa ce ta fi ba ka sha’awa, sannan wacce ce ta fi ba ka al’ajabi? Ya amsa da cewa:
“In dai a kada mutum ne, to kayin kokowa nufin Allah ne. Ka san kura da ta taka kwado sai ta ce sa’ar kafa; ba don shi ta fito ba, amma kuma ba za ta bar shi ba. Ka san kayin da Laminu Mai Dabba ya yi bara, wanda ya ci takobi, sa’ar kafa ce, domin bai yi tsammanin zai yi kayi ba amma sai Allah Ya ba shi sa’a. Haka kuma sanda wata ’yar shamuwa ta Jihar Difa, watau Kari Bulaye, ya kada Kadade, wanda shi ma bai yi tsammanin zai yi kayi ba, amma sai ga shi ya yi. Saboda haka, abin daga Allah yake. In da mutum ne yake ba da takobi, to tun da aka fara kokowar takobi da Kadade zan bai wa. Don bai da kashe ni ka diba, amma yanzu kana ganin ’yan kokowa kowa lake da aljihunsa kusa da jikinsu. Wadannan ya zan iya samun kudi daga wajensu. Amma shi Kadade, in ya samu kudi ni yake bai wa. Kuma har ya ce mini in tafi gidansu in yi roko. Da na je, dabba goma sha bakwai ya ba ni, akuya shida da tunkiya biyar da shanu biyar da rakumi da kudi jaka maitan da santolo shida da hatsi. Ai Adarawa ba su haifi da kamar Kadade ba.”
(10)-Sani dan Indo. An tambaye shi cewa: Idan muka dawo kan ita wannan sana’a ta waka, me ya ba ka sha’awa kuma ya ja ra’ayinka har ka zabi ka zama mawaki? Ya amsa da cewa:
“Wannan sana’a ta waka dai ba gadonta na yi ba, abin da na gada ita ce sana’ar Fawa. Gidanmu na daya daga cikin masu sarautar Fawa a Gusau. Kamar yadda na fara gaya maka da farko, ina dan shekara bakwai, a lokacin nan ina tallar tsire. Duk lokacin da Sani Kaka Dawa ya zo da jama’arsa yana wasa, sai kawai in ji a raina cewa wannan tallar tsire ba ta yi mini ba, sai na ji kawai ina sha’awar sana’ar nan da Sani Kaka Dawa yake yi, watau kida da waka. Tun ina zuwa kallon wasan nasu, har na yanke hukuncin shiga sana’ar. Lokacin da na fara bin su kuwa, ba su wulakanta ni ba. Haka na fara tafiya tare da su har iya lokacin da na fara cin gashin kaina. Na samu kimanin shekara tara tare da Sani Kaka Dawa, ban iya waka ba, sai dai in yi masa kida da kuma amshi.”

ADAM A ZANGO



  • BA kamar Zangon Daura ko Unguwar Zango Bare-Bari da ke cikin Jihar Kano ba, wa]anda wurare ne da suka yi suna a tarGhin }asar Hausa, Zango Kataf gari ne wanda yawancin mazaunan sa }abilar Katafawa ne. garin ya yi }aurin suna kuma ya ajiye mummunan tarihin fa]an }abilanci da na addini inda aka kashe ]aruruwan mutane. A wannan garin ne aka haifi Adamu Abdullahi, ko kuma mu ce Adam A. Zango, fitaccen jarumin nan da aka sani da la}abin ‘Usher’.


    A lokacin da aka yi rikicin Zango }ataf, Adam yana yaro }arami inda yake karatu a makarantar ‘Zango 1 Primary School.’ A hirar da ya yi da wakilinmu, jarumin ya labarta mana cewa, "Lokacin da rikicin kashe-kashen Zango Kataf ya ~arke, ni ina }arami, kusan ban san komai ba. Sai ma ~oye ni da aka yi kamar yadda aka ri}a ~oye sauran yara }anana".


    A nan sai Adam ya sunkuyar da kai ya tuna abin da ya gani a lokacin rikicin. "Ka san bayan an yi kwanaki ana rikici, to daga bisani ‘yan sanda sun zo suka tcsirar da mu daga harin {atafawa. To a gafen titi na ga tulin gawarwaki birjik, har da na wa]anda na sani."


    Ba wannan bala’in ka]ai Adam ya gani ba. Ya }ara da cewa ya ga yadda aka ri}a banka wa gidaje wuta suna }onewa }urmus.


    Adam ya }ara da cewa daga nan ne wani kawunsa mai suna Alhaji Rabo Musa Salisu ya ]auke shi tare da sauran dangi ya ranga]a da su garin Jos. Ko Adam ya san gwarzon Katafawa wanda aka yi wa shari’a bisa zargin shi ne ummulhaba’isan kisan kiyashin da aka yi, wato Janar Zamani Lekwot, ido da ido kuwa? "A’a, ni ban san shi ba, sai dai sunansa da kuma aika-aikar da ya aikata kawai na ke ji, inji Adam.


    Adam bai da]e a garin Jos ba sai kawunsa ya sa shi makaranta. A Turance, ya ce mana, "I was enrolled in Islamiyya primary school. When I finished, I was later admitted at Government Secondary School, Laranto." wato yana nufin ya yi karatun Islamiyya, da ya gama aka saka shi a makarantar Sakandaren Gwamnati ta Laranto.. Kun san a industiri akwai magulmata masu cewa wai Adam Bakatafe ne, ya saje da Hausawa yana yin fim. Har ma wasu na cewa ba su san ma’anar ‘A’ ]in nan ta tsakanin sunansa ba.


    Da aka yi masa tambaya kan ha}i}anin gaskiyar salsalar sa, sai Adam ya gyara zama ya ce, "To yau dai tun da an tambaye ni, bari in fa]a ga duk wanda ya damu ya sani ko ya ji. Ni dai Bahaushe ne cikakke, ba Bakatafe ba."


    Ya ci gaba da cewa, "Da farko, kakana zuwa Zangon Kataf ya yi, daga shi kuma mahaifina ya ha]u da mahaifiya ta ne a Saminaka, suka yi aure, suka dawo Zangon Kataf da zama, inda aka haife ni."


    Adam ya }ara bin tushensa inda ya ala}anta kansa da jinin Larabawan Shuwa. "Kai, ni fa akwai jinin Shuwa Arab a jiki na, domin mahiifiya ta tana da jinin Shuwa Arab ajikinta".


    A halin yanzu Adam ya dawo da mahaifiyarsa Kano inda ita ma take ]an]ana romon ribar industiri. "Ni ban ga dalilin da zai sa in bar mahaifiya ta can nesa ba, na fi so in matso da ita kusa da ni. Kuma na gode Allah da azurtawar da a yi min. don haka wajibi na ne in kyautata wa mahaifiya ta."


    To mu ci gaba. Da yake Adam (komu ce Adamu) bai yi nufin ci gaba da karatu ba, yana kammala karatun sakandare a Laranto, sai ya tarkato kayansa ya nufo Kano, kaitsaye ya zarce gidan buga wa}o in fina-finai na ‘Lenscope Media’ mallakar furodusa/darakta Sani Mu’azu, wanda shi ma ]an Jos ne.


    "Shekara biyu na yi ina cin ba}ar wahala a ‘Lenscope Media’ inji Adam. "Haka nake zaune ina kallon kaina a matsayin jarumi, amma har zuci na san ni ba jarumin ba ne, saboda idan na yi sin ]aya, ban san ranar sake yin wani ba."


    Yana cikin irin wannan zama ne sai sakatariyar kamfanin Lenscope ]in, mai suna Hauwa M.D. (Kun tuna ta?) Ta fara tausaya masa ganin cewa matashin ]an fim ]in yana cikin halin rayuwar na ware-ga-dangi. Sai ta ba shi shawarar me zai hana ya koyi yadda ake ki]a, wato buga wa}a.


    Da farko Adam bai ]auki shawarar ba, sai ya nuna mata cewa, "Ni fa na zo Kano ne don in zama jarumi in yi fim, ba in buga wa}a ba."


    Amma da ya ga uwar bari, kullum mafarkin zaman sa jarumi na }ara faskara, sai ya nemi fitaccen maka]in nan Ibrahim Danko ya ri}a koya masa yadda ake buga wa}ar a Lenscope ]in. "Gaskiyar magana ka ji yadda aka yi na zama maka]i ba a son raina ba."


    Cikin }an}anen lokaci aka san Adam A. Zango a matsayin maka]i, domin ya buga wa}o}in fina-finai masu yawan gaske.


    Shin ya ya aka yi bayan ya zama mashahurin maka]i kuma ya riki]e ya zama fitaccen jarumi?


    Ya ba mu labarin: "To da na tara ku]in da zan iya yin fim, sai na yi tunanin in yi fim nawa kuma in zama jarumin fim ]in nawa tunda matsayin jarumi."


    Da wannan ne ya yi fim ]in sa na farko a matsayin jarumi mai suna ‘Surfani.’


    Adam ya yi suna a fina-finan soyayya, musamman fim ]in sa ‘Raga, wanda a yanzu ake kiran sa da suna fim ]in, wato Mai Raga. Amma ‘Zabari,’ Kallabi’ da irin su ‘Kawanya’ ne suka fara fito da shi. Wannan tashe da ya yi kuwa ya sa Adam ya yi wa matasa masu buga rol na soyayya zarra. Ko a gida ko a lokeshin ko a fim, inda Adam yake za a gan shi ‘yan kallo suna baibaye shi. Ofishinsa na buga wa}a mai suna ‘Crown Studio’ kuwa wata matattara ce ta matasa maza da mata. Sai dai kuma duk da wannan, shi Adam muradinsa tun farko shi ne ya zama wani tantirin ma}etaci, ]an daba, bos, irin su Shu’aibu Kumurci.


    To ya ya aka yi ya zama jarumin soyayya?


    Ya ce, "Gaskiya Ali Nuhu ne zan iya ce malamina. Shi ya koya min yadda ake yin rol na soyayya. Kai, sai da ta kai Ali kan zaunar da ni yana koya min yadda zan ri}a yin kukan jimamin soyayya a fim. To yanzu ga shi ina jin da]in wannan rol ]in, don ya kar~e ni."


    Shin Adam yana sane da yadda ‘yan mata ke yi masa son daga-nesa-nesa kuma masu yawan bugo masa waya fa?


    Sai ya amsa da cewa, "Ai ina sane, mahaifiyata ce ke ce min in ri}a yin kaffa-kaffa da ‘yan matan zamani. Shi ya sa ma take ta bi na da lallami cewa in yi aure kawai ko sa shafa min lafiya."


    To Adam A. Zango muna jiran mu ga wannan rana ta aurenka. Haka su ma ‘yan matan naka, suna jira

ALI NUHU

  1. ALI HUNU
  2. Ra’ayi muna son Ali Nuhu ya bayyana mana takaitacen tarihin rayuwarsa ?
  3. Ali Nuhu : Ni dai dan Najeriya ne, an haife ni a shekarar alif dari tara da saba’in da hudu(1974) a jahar Barno cikin garin Meduguri, daga nan na girma a cikin jahar Kano inda a nan na yi karatuna na pramare da sakandre, daga bisani na karasa a university ta garin Jos, sai na tafi bautar kasa a Ibadan, daga nan na dawo jahar Kano inda na fara shirya fina-finan Hausa.
  4. Ra’ayi : miye yaja ra’ayin ka har ka shiga shirya fina-finan Hausar ?
  5. Ali Nuhu : To’ ni dai tun ina karami ina kallon fina-finai irin na Indiya, da na turawa, tare da kallon wasannin kwaikwayo na hausa irin na su Kasimu Yaro da dai sauransu, da yake nima ina da ra’ayin in na girma in dinga yin irin wannan wasa, sai gashi kuma bayan na girman Allah ya cika mani burina na fara yi.
  6. Ra’ayi : ko wace irin sana’a da farko bata rasa wahalhalu kafin a cimma ribarta, ko zaka iya fada mana wahalhalun da ka sha karo da su, kafin ka kai ga wannan matsayi da kake a halin yanzu ?
  7. Ali Nuhu : E’ to gaskiya ba a rasa wahalhalu a kowace irin sana’a, wahala ta farko da na fara fuskanta ita ce, lokacin da ina sabon shiga akasari mu sabin yan wasa mu kan bi kofa-kofar kampanonin shirya fina-finai da sunan ziyara, ko hira, domin dai kar a manta ka.Abu na biyu kuma dazan iya cewa mai wahala shine, lokacin kasan babu wayar Salula balantana in ana neman ka nan take a yi amfani da ita a san inda kake, dan haka da an neme ka domin ka taka wani Sin ba a same ka ba to shi kenan, ana ganin wani sai ayi amfani dashi.
  8. Irin wadannan matsaloli sune zan iya cewa matsalolin da na dan fuskanta a farkon shigata harkar fim.Amma a halin yanzu sai dai mu ce mun godewa Allah, mun godewa manyan mu da muka samu a cikin wannan haraka, domin basu nuna mana bakin-ciki ko kyashi ba, sun nuna yakamata muma mu shigo a yi damu kuma Alhamdu Lillahi an samu biya bukata, gashi kuma har Allah ya kawo mu wannan matsayi. Ra’ayi : masana yare da al’adun hausa na ganin fina-finan da kuke yi basu da alaka da al’adun hausawa, balantana su ciyar da yaren ko al’adun hausar gaba, ganin irin yadda ku ka cakuda al’adun turawa da na indiya a cikin na hausa ko mi zaka ce anan ?
  9. Ali Nuhu : To ni a kulum irin wadannan mutane abinda na ke nuna musu shi ne, in a kace al’ada ana nufin yanayin zamantakewa da kuma rayuwa mutum ta yau da kulum, to in kace an kaucewa tsarin al’ada ta bahaushe, sai a tambayeka minene aka yi wanda ya kaucewa al’adar bahaushe. Na san dai watakila suce rawa da waka da ake yi, to bahaushe dai yana rawa da waka ba tun yanzu ba tun a da can baya, abinda kawai mutum zaice shine, tsarin yadda ake rawa da waka a da ba irin na yanzu bane, domin komai yanzu an riga an sa cigaba a cikinsa, ko a makarantar Allo inka ka dauka a da a fili ake tara almajirai a hada itace a kunna wuta su kewaya suna karatu.
  10. Yanzu kuma ka gani a cikin Aji ake koyar da su, a kan tebura da kujeru ko ba haka ba ? ka gani kenan al’adar ta canja bisa yadda ake yinta a da, to haka ne canjin yanayin rayuwa aka samu a ko ina. Wani misali in ka dauki bahaushen mutum a zamanin yanzu musamman matashi, kashi 90 cikin 100 zaka ga yana sanye ne da wandon Jins da dai sauran sutura irin na turawa, to kaga yanayin al’adar bahaushe kenan ta yanzu, amma kuma a da can baya ba haka yanayin al’adar bahaushe take ba. Ni da dai irin wadannan mutane za su rika cewa ne, a rinka tuno da al’adunmu na hausa na can baya dan kar su gushe harma a manta da su, wannan bai zama laifi ba, amma ba wai suce an kaucewa al’ada ba, yadda rayuwarka take ai shine al’adarka.
  11. Ra’ayi : Dan mi a cikin fina-finanku ku ka fi kwaikwayon fina-finan Indiya da na Amerika ?
  12. Ali Nuhu : Yanzu ka dauka kasashe irin su Najeriya da Nijar duk ba siyasa ake ba ? siyasar da ake yi ba irin ta turawa bace suka kwaikwaya suna yi ba ? mi yasa baza a kirkiro da wata siyasa ba a ce gata siyasa ce irin ta yan Nijar ko yan Najeriya mu daina amfani da irinta turawa, amma ka gani ba a yi ba sai irin tasu din dai muke yi.
  13. Ai komi da ke faruwa yanzu a duniya an riga an ayyana a rai, turawa su suka cigaba saboda haka komi da ake kokarin yi ana kokarin yin irin nasu ne,kai bamu hausawa ba ma, ka dauka balarabe da yake da akida da ra’ayi kan al’adunsa da addinin sa kwaikwayon ba’amurke yake, shiga irin tasa da sauransu, to abu ne da zamani ya taho dashi, kuma a gaskiya a wannan lokaci da muke ciki in kana son a ce ana yi da kai doli ne ka bi wannan zamani, idan kuma ka ki to gaskiya ba za ka kai labari ba.
  14. Ra’ayi :Ana zargin Ali Nuhu da girman kai, da kuma wulakanta mutane, mine ne gaskiyar lamarin ?
  15. Ali Nuhu : Yayi dariya ! yace to kasan dai bahaushe yace gani ya kori ji, kuma a zahirin gaskiya ni abinda zance akan wannan shi ne, zan fi so in muka gana da mutum, sai ya yankewa kansa hukumci in yaga yanayin yadda muka yi mu’amala dashi, domin yanzu zan iya fadar abu ya kasance na fada ne dan in gyara kaina ko makamancin haka, gara dai mu hadun in muka hadu da mutum ka gani shi sai ya yankewa kansa hukumci.